1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rashin ci gaba a arewacin Afirka ta Tsakiya

Usman ShehuMarch 28, 2013

Daga Arewa maso gabashin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya sabon shugaba Michel Djotodia ya fito. Amma kuma yankin da ke da iyaka da Chadi da kuma Sudan na fama da karancin kayayyakin more rayuwa.

https://p.dw.com/p/186Ol
Hoto: DW/Cécile Leclerc

Da ma dai al'umomin yankin arewa maso gabashin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya sun dade suna kokawa game da komabayar da suke fuskanta. Ko da gamayyar Kungiyoyin tawaye ta Seleka da ta kwace mulki, sai da ta zargi gwamnatin Bozize da yi wa yankin rikon sakarnar kashi. Su ma dai masu sa ido a harkokin zabe ba su sami damar isa wannan yanki ba a shekara ta 2011, saboda zama ruwan dare da fashin makamai ya yi. A cewar Adolphe Ngouyombo, shugaban kungiyar kare hakkin bani Adama da taimakon jin kai ta Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, dalilai da dama ne suka jefa wanyin cikin hali da ta ke ciki a yanzu.

"Wannan ya samo tushe ne tun lokacin da kasar ta samu 'yancin kanta daga turawan Faransa. Wannan ya na da nasaba da yanayin yankin. Baya ga nisa, a damuna ba a samun damar shiga ko fita."

Flüchtlinge in Mali
Mutane da dama na tsarewa yankin arewacin jamhuriyar Afirka ta TsakiyaHoto: picture-alliance/dpa

Ma'amala tsakanin yankin da Chadi da Sudan

Sai dai kuma yanki na Arewa maso gabashin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya na da iyaka da kasashen Chadi da Sudan da kuma Sudan ta Kudu. Yankin ya yi kaurin suna a sigar fataucin muggan makamai. Kazalika 'yayan wannan yankin da ake damawa da su a harkokin siyasa da ma dai na mulki ba su taka kara sun karya ba. Su na ma daga cikin rukunin wadanda suke da karancin iya karatu da kuma rubutu. Sai dai kuma al'amuran sun fara inganta a shekarun baya-bayannan sakamakon dauki da suke samu daga kungiyoyin jin kai na kasashen waje. Amma kuma ma'amala tsakanin kabilun wannan yanki na nan daram dakam duk kuma da rikicin tawaye da kasar ta saba cin karo da shi. Daidai a cikin gamayyar kungiyoyin tawaye ta Seleka, ana samun 'yayan wannan yankin da ke jin harshe fiye da daya, a cewar Adolphe Ngouyombo

Markt Zentralafrika Bangui
Matan Jamhuriya Afirka ta Tsakiya na kokarin rike kansu da kansuHoto: Sia Kambou/AFP/Getty Images

"A kan iyaka dai jama'a na yin magana ne cikin harsuna biyu. A nan ba wai sango da daukacin 'yan jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ke ji ba ne kawai harshen ma'amala. Amma suna magana ma cikin harshen larabci. A yanzu dai abu ne mai matikar wuya a yi bayani game da yawan wannan yani a gamayyar kungiyoyin tawayen Seleka. Amma a bin da ya fito fili daga binciken da na gudanar jiya shi ne cewa akwai musulmai da dama a cikin gamayyar."

Daga Arewa maso gabas Djotodia ya fito

Shi ma dai Michel Djotodia da ya ayyana kansa a matsayin sabon shugaban Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya dan asalin garin Birao da ke wannan yankin ne. Yayin da shi kuma firaminista Nicolas Tiangaye ya fito daga tsakiyar Jamhuriyar afirka ta tsakiya, a cewar Ngouyombo.

"Shugaban dan sasalin yankin Arewa maso gabas ne. Amma dai firaminista ya fito ne daga Gouam da ke tsakiyar kasar musamman ma daga garin Bouca."

Michel Djotodia
Shugaba Michel Djotodia dan asalin yanki ne da ke fama da talauciHoto: Getty Images

Gaggwarmaya da Tiangaye ya ke yi wajen kare hakkin bani Adama da kuma mutunta yarjejniyar zaman lafiya da gwamnati da 'yan tawaye suka cimma a Libreville na daya daga cikin dalilan da suka sa aka bai wa firaministan damar ci gaba da rike wannan mukami na firaminista a Jamhuriyar Afirka ta tsakiya.

Rahoto cikin sauti na kasa

Mawallafi: Mouhamadou Awal Balarabe
Edita: Mohammad Nasiru Awal