Rasa rayuka a Bangaladesh sakamakon siyasa
December 30, 2018Talla
Jami'an 'yan sanda sun yi nasarar harbin uku daga cikin wadanda suka tada rikici bayan sun hallaka dan sanda guda. Alamu na nuni da cewar Firaminista Sheikh Hasina za ta iya samun nasarar ci gaba da rike mukaminta a karo na hudu
Sai dai duk da samun yabn da Firaministar ke samu daga ciki da wajen kasar sakamakon farfado da tattalin arzikin kasar da kuma karbar 'yan gudun hijira daga kasar Myanmar, masu hamayya da mulkinta na zarginta da hana adawa a fadin albarkar baka a fadin kasar.
A nata bangaren hukumar zaben kasar ta bayyana cewar idan bincike ya tabbatar da samun aringizon kuri'u kamar yadda 'yan adawa suka zarga, babu shakka hukumar za ta dauki matakin da ya dace.