1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rantsar da wakilan kotun tsarin mulki a Nijar

March 25, 2013

Wannan sabuwar kotun, ita ce ta maye gurbin tsohuwar kotun tsarin mulkin da ta taka birki ga shirin ta zarce na tsohon shugaba Tanja Mammadu.

https://p.dw.com/p/183uP
Gebäude des Parlaments der Republik Niger, Niamey. Foto: Mahaman Kanta/DW, 19.5.2011, Niamey / Niger, Zulieferer: Thomas Mösch
Hoto: DW

Kotun tsarin mulkin kasar ta Nijar ta kunshi mambobi bakwai wadanda suka hada da wakilin shugaban kasa da na fadar shugaban majalisar dokoki da na kungiyar malaman jami'a da na kungiyoyin farar hula da ke fafatukar kare hakkin bil Adama a Nijar. Sai kungiyar lauyoyi wadda ke da wakilcin mutun guda sai kuma ta alkalai dake da wakilai biyu, Bayan an rantsar da su a bisa littafin addinin ko wane daga cikinsu.

Bikin kaddamar da mambobin kotun tsarin mulkin ya samu halartar
jakadun kasashen waje da ke aiki a Nijar da 'yan majalisar dokoki da wakillan kungiyoyin farar hula da na jam'iyyun siyasa. Da suke tsokaci kan wannan sabuwar kotun tsarin mulki kawancen jam'iyyun adawa na ARN ta bakin kakakinsa Malam Lawal Amadu bayyana fata ta yi na ganin kotun za ta zare gaskiya cikin aikinta. To amma daga nashi bangare Dr Naray daya daga cikin mambobin kotun tsarin mulkin da aka rantsar fata ya yi Allah Ya kama masu su iya kai wadannan kaya da suka dauka.

A nan gaba mamboobin kotun za su zama na musamman domin zaban shugaba da mataimakinsa daga cikinsu.

Wer hat das Bild gemacht?: Mahaman Kanta (DW Haussa) Wann wurde das Bild gemacht?: 2009 Wo wurde das Bild aufgenommen?: Iférouane, Niger Bildbeschreibung: Bei welcher Gelegenheit / in welcher Situation wurde das Bild aufgenommen? Wer oder was ist auf dem Bild zu sehen? Brigi Rafini (andere Schreibweisen des Vornamens: Birgi, Birji) wurde im April 2011 vom neuen Präsidenten des Niger, Mahamadou Issoufou, zum Ministerpräsidenten der ersten demokratischen Regierung nach dem Militärputsch von 2010 ernannt. Er war zuvor Abgeordneter der Nationalversammlung und Bürgermeister der Stadt Iférouane im Norden des Landes. Rafini gehört der Volksgruppe der Tuareg an. In welchem Zusammenhang soll das Bild/sollen die Bilder verwendet werden?: Artikel
Praiminista RafiniHoto: DW

Mawallafi : Gazali Abdu Tasawa
Edita : Zainab Mohammed Abubakar