1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ramaphosa ya koma gida saboda rikici

Yusuf Bala Nayaya
April 20, 2018

Shugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kudu ya katse babban taron kasashe rainon Birtaniya na (Commonwealth) don komawa gida ya fuskanci matsalar masu bore da zanga-zanga kamar yadda ofishin shugaban ya bayyana.

https://p.dw.com/p/2wNIm
Südafrika - neuer Präsident Cyril Ramaphosa
Hoto: Getty Images/AFP/M. Hutchings

Shugaba Ramaphosa da ya karbi mulki a watan Fabrairu bayan ya sha alwashi na farfado da tattalin arzikin kasa da murkushe ayyukan masu cin hanci da rashawa ya ce zanga-zangar da ke wakana a lardin Arewa Maso Yamma na kasar inda ake gwabzawa da 'yan sanda lamari ne da zai yi illa ga kasar don haka sai ya yi kira da kwantar da hankula a koma tattaunawa.

Ramaphosa ya dai yi kira ga 'yan sanda su yi taka tsantsan kar a yi amfani da karfi da ya wuce kima yayin da masu zanga-zanga suka farwa shaguna suna dibar kayan jama'a a wannan zanga-zanga da ke da nasaba rashin aikin yi da tsadar gidaje da karuwar cin hanci da rashawa a kasar. Lamarin dai na nuna babban kalubale da ke gaban sabon shugaban.