Nijar za ta yaƙi Boko Haram
February 6, 2015Talla
Matakin da ke zuwa a dai dai lokacin da mayaƙan Boko Haram ke kashe-kashe a kan iyakokin Najeriyar da makwabtan nata, mahukuntan na Nijar na ganin zai buɗe kafar tinkarar ƙungiyar gaba-gadi daga arewaci.
Boko Haram dai ta kashe sama da mutane ɗari a Larabar da ta gabata, ciki har da soji 19, a wani harin da ta ƙaddamar a garin Fotokol da ke iyaka da Najeriya.
Mawallafi Muntaqa Ahiwa
Edita Abdourahamane Hassane