1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar za ta yaƙi Boko Haram

February 6, 2015

Rahotanni daga birnin Yamai na jamhuriyar Nijar, na cewar gwamnatin Nijar ta shirya tura dakarunta zuwa Najeriya don yaƙar Boko Haram.

https://p.dw.com/p/1EWY2
Niger Präsident Mahamadou Issoufou
Hoto: Seyllou/AFP/Getty Images

Matakin da ke zuwa a dai dai lokacin da mayaƙan Boko Haram ke kashe-kashe a kan iyakokin Najeriyar da makwabtan nata, mahukuntan na Nijar na ganin zai buɗe kafar tinkarar ƙungiyar gaba-gadi daga arewaci.

Boko Haram dai ta kashe sama da mutane ɗari a Larabar da ta gabata, ciki har da soji 19, a wani harin da ta ƙaddamar a garin Fotokol da ke iyaka da Najeriya.

Mawallafi Muntaqa Ahiwa
Edita Abdourahamane Hassane