1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar:'Yan adawa sun kaurace wa tattaunawa

Mahaman Kanta AH
January 23, 2019

Manyan jam'iyyun siyasa na Jamhuriyar Nijar wadanda suka hada da FRDDR, da Front Patriotique sun ki halarta taron tattaunwa don neman sulhu a tsakanin 'yan siyasar a kan batun zabe.

https://p.dw.com/p/3C3cp
Niger Wahlen Kandidat Ibrahim Yacouba
Ibrahim Yacouba shugaban jam'iyyar MPN Kishin Kasa daya daga cikin shugabannin 'yan adawarHoto: I. Sanogo/AFP/Getty Images

Wannan ba shi ne karo na farko da ake samun baraka tsakanin jam'iyyun siyasar na adawa da jam'iyyun da ke yin mulki a game da batun shirya zaben shugaban kasa da na 'yan majalisun dokokin da ake shirin yi a nan gaba. An shirya firaministan kasa Birji Rafini, a ranar  Alhamis(24-01-19) zai jagoranci zaman taron majalisar sassanta rikicin siyasar watau CNDP domin kaddamar da sakamakon aikin kwamitin da ya yi nazarin gyaran fuskan kudin zabe. Hadin gwiwar manyan jam'iyyun kawancen adawar kasar watau FRDDR, da Front Patriotique, sun ce ba za su halarci zaman majalisar ba.