1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar alkalai ta kalubalanci gwamnati

Mahaman Kanta RGB
August 7, 2019

Takun saka ya kunno kai tsakanin Kungiyar Alkalai ta SAMAN da gwamnati dangane da nade-naden mukamai da canza guraben aikin alkalan ba bisa ka'ida ba

https://p.dw.com/p/3NWg3
Niger Treffen der afrikanischen Union in Niamey - Mahamadou Issoufou
Hoto: AFP/I Sanogo

Barakar ta kunno kai a Jamhuriyar ta Nijar, bayan da Kungiyar Alkalai ta SAMAN ta zargi gwamnati dangane da nade-naden mukamai da canza guraben aikin alkalan, inda kungiyar ke zargin gwamnatin da nuna mata wariya batun da bangaren gwamnatin ya musanta.

Kungiyar ta SAMAN ce ta fito ta kuma kalubalanci gwamnatin Nijar, a game da batun nade-nade da tade-taden alkalai da aka yi a karshen makon jiya. A cikin wani taron manema labarai da suka kira a ranar Talatar da ta gabata, Kungiyar ta SAMAN ta ce,  za ta zage damtse don kawo karshen wadannan matsaloli, koda ya ke a wani taron 'yan jarida da ya kira ministan shari'ar kasar ya musanta wadannan matsalolin da ake magana a kai.