1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An nemi gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta saki 'yan gwagwarmaya

Abdoulaye Mamane Amadou
May 22, 2018

Wasu kungiyoyin kasa da kasa masu fafatuka sun saka kaimi ga gwamnatin Jamhuriyar Nijar saboda neman sakin 'yan fararen hula a wata budaddiyar wasikar da suka aike ga shugaban kasar.

https://p.dw.com/p/2y8JB
Niger Polizei in Niamey
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

 

Kimanin kungiyoyi 8 zuwa 10 ne kawo yanzu na fafatukar kare hakin dan Adam daga kasashen duniya suka aike da wasikun walau na nuna rashin jin dadinsu game da ci gaba da tsare jiga-jigan kungiyoyin fararen hular nan a gidan yari ko kuwa nuna rashin amicewa game da batun da suka kira hana 'yanci da walwalar fadin albarkacin baki da 'yancin da kundin tsarin mulki da dokoki na duniya suka tanada na shirya zanga-zanga.

Niger Protest gegen das Haushaltsgesetz der Regierung
Hoto: Getty Images/AFP/B. Hama

Sakon baya-bayan nan ya fito daga kungiyoyin Amnesty wace ta yi kira ga a saki 'yan fararen hular hakan da hadin gwiwar kungiyoyi na Tournons la Page da suka aike da wata budaddiyar wasika ga shugaban kasa.

Niger Präsidentenpalast
Hoto: DW/M. Kanta

Duk kokarin jin ta bakin hukumomi kan wannan batun haka ta kasa cimma ruwa domin kuwa har an tuntubi kakakin Gwamnatin Nijar yaki ya amsa waya sai dai a can baya a wata hira da DW Ministan cikin gidan Jamhuiyar Nijar Malam Bazoum Mohamed ya ce daukacin 'yan kungiyoyin fararen hula da aka kama ne suka bai wa gwamnati damar kama su da laifi saboda sun aikata zanga-zangar da gwamnatin ta haramta,