1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nakiya ta hallaka fararen hula a Mali

March 31, 2013

Ba a bayyana yawan mutane da tashin nakiya ya yi awan gaba da rayukansu ba a arewacin Mali. Amma kuma wani harin kunar bakin wake ya jikata wani soja a wannan yanki.

https://p.dw.com/p/187Ly
Malian troops secure the area where a suicide bomber blew himself up, next to an Islamist sign, in the northern city of Gao, Mali, February 10, 2013. Malian troops foiled a second suicide bomber attack in the northern town of Gao late on Saturday, highlighting fragile security in zones recaptured by a French-led offensive that is hunting Islamist insurgent bases further north. Malian Captain Sidiki Diarra told reporters that besides the bomber, who was blown to pieces, one Malian soldier was lightly wounded in the attack. REUTERS/Francois Rihouay (MALI - Tags: MILITARY CONFLICT)
Hoto: Reuters

Wani dan kunar bakin wake da ya tayar da bam ya jikata wani soja a garin Timbuktu na arewacin kasar Mali.Jami'ai sun ce cikin wani lamarin na daban tashin nakiya da a ka binne, ya hallaka wasu fararen hula uku. Wannan na faruwa ne lokacin da Shugaban Faransa Francois Hollande ya bayyana cewa an cimma muradun da a ka saka a gaba a arewacin Mali, sannan za a fara janye dakarun kasar na ba da dadewa ba.

Dakarun na Faransa sun taimaka wajen sake kwato yankin arewacin kasar ta Mali daga hanun 'yan tawaye masu alaka da kungiyar al-Qaeda.Ita dau Mali ta fada hannun masu kaifin kishin addinin Islama bayan da sojoji suka kifar da gwamnatin Toumani Toure.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe