1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya ta samu zuba jari fiye da kowa a Afirka

Usman ShehuApril 2, 2013

Rahoto ya nuna cewa a nahiyar Afirka, Najeriya ce ke kan gaba a samun masu zuba jari daga ƙasashen waje a bana

https://p.dw.com/p/188Oj
ABUJA, NIGERIA - DECEMBER 20: In this handout image provided by the International Monetary Fund (IMF), talks with Nigerian Central Bank Governor Sanusi Lamido Sanusi (L) during a joint press conference December 20, 2011 in Lagos, Nigeria. Lagarde is on her first trip to Africa as the Managing Director and will also visit Niger. (Photo by Stephen Jaffe/IMF via Getty Images)
Gwamnan Babban bankin Najeriya Sanusi Lamido Sanusi ke ganawa da shugabar asusun IMF Christine LagardeHoto: Getty Images

Kwararar da jarring daga kasashen wajen ke ci gaba da yi zuwa ga tattalin arzikin Najeriya da shekaru uku kenan a jere yake ci gaba da karuwa musamman a sashin bankuna, samar da wuta lantarki da man fetir a kasar, fanonin da a yan shekarun nan suke samun karuwar masu rigegen zuba jari a cikinsu, musamman saboda mayar da su a hannun yan kasuwa.

Wannan lamari da ke kara mayar da Najeriyar tamkar wata budurwar da ake rige-rige a kanta a fannin zuba jarin duk kuwa da irin kalubale na rashin isassun kayan aiki da kasar ke fuskanta da ma matsalolin tsaro. Abinda ya sanya ministar kula da ciniki da zuba jari a Najeriyar Dr Olusegun Aganga bayyana cewa akwai fa dalilin da ya sanya faruwar hakan, saboda Najeriya na cikin kasashe biyar da cibiyar zuba jarin kasa da kasa ta bayyana wadanda suka fi daukan hankalin masu zuba jari a duniya.

LAGOS, NIGERIA - JULY 15: A detail of some Nigerian Naira,(NGN) being counted in an exchange office on July 15, 2008 in Lagos, Nigeria. (Photo by Dan Kitwood/Getty Images)
Wani ke ɗan Najeriya ke ƙirga NairoriHoto: Getty Images

‘'Yace idan ka duba Najeriya ka kwatanta da sauranm kasashe, za ka ga cewa kasa ce da ke da yanayin da ke samar da bunkasar jarin da ka zuba tare da samun riba. Kashi 75 cikin ɗari na kasashen duniya a yanzu suna da yanayin na koma bayan ribar da ake samu a cikinsu, wannan ya sa muke samun ƙarin jarin da ke shiga kasar a fannoni da dama, don haka muna da kyakyawan yanayi domin ciyar da kasar gaba zuwa mataki da ya kamata ta kasance''.

Duk da irin wannan ci gaban da Najeriyar ke samu a yanzu da bayanai daga hukumar sa ido a kan jarin da ake zubawa a kasashen Afrika ya nuna Najeriya a matsayin wace ke kan gaba da kasashen da dama, domin daga jarin da aka zuba a tattalin arzikin kasar na Dalla bilyan shida a shekara ta 2011 da a yanzu ya karu zuwa Dalla bilyan tara a wannan shekarar, ya sanya kasar zama kan gaba a wannan fani cikin nahiyar Afirka.

To sai dai kalubalen da masana harkokin tattalin arzikin da ci gaban kasa ke ganin na gaban Najeriya shine maida hankalin domin yan kasa su ci moriyar jarring da ke shiga kasar, don gujewa mayar das u gugar yasa, abinda ya sanya Malam Ahmed Rabiu masani a fabnin tattalin arziki da harkar zuba jarri bayyana cewa.

Ölindustrie in Nigeria verursacht Umweltprobleme Jan 19, 2005; Port Harcourt, Rivers State, NIGERIA; Air pollution is widespread in Port Harcourt, the oil and gas capital of Nigeria. On December 25, 2004 an oil pipeline ruptured in the Orere Uluba community, causing extensive environmental damage. Shell and the community agreed to a cash settlement of 250,000 Naira (approximately $1900 USD) to compensate for harm done. Shell and the Orere Uluba decided jointly to clean up the spill. However, Shell employees and Nigerian federal security forces went in four days earlier than planned in effort, to mask damages and prevent community documentation of the spill. Mandatory Credit: Photo by Mark Allen Johnson/Press +++(c) dpa - Report+++
Wasu talakawan Najeriya dake shaƙar hayaƙin masana'antuHoto: picture-alliance / dpa

‘'Yace watau saboda rashin samun saita al'amarin wadanda suke rike da hukumomin da y a kamata su tabbatar da an yi dai dai, daga maikatan da mu kanmu yan kasuwa, har yanzu ba'a kamala wannan saitin ba, cin hanci da rashawa da sama da fadi da kudin alumma, da rashin tausawa masu da rashin tunanen matsayin da Najeriya take ciki a lokacin da aka kawo wani abu na sauyi. Kullum ya kamata a sani muna nan milyan 160, amma wadanda suka fahimci inda aka dosa basu wuce milyan biyu ba, wadanda suke zuwa kasashen duniya suke ganin su san al'ammura basu wuce rabin milyan ba, amma in an tashi za'a yi wani abu sai dauko wanda yafi kowane ci gaba a duniya a ce shi za'a yi wannan ba dai dai bane''.

Amma ga Dr Sule Bello na jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria da ya kasancce kwarrare a fanin ci gaban kasa da kasa yace dole a koma tsarin da aka baro a shekarun baya, domin ganin tasirin lamarin.

‘'Hanya da za'a bi ba wai da fada ba, bada zage-zage ba, ai ka ga mu muke da iko da kanmu dole, a fita kasashen waje in zamu sayi kaya, mu saya in ba haka ba mu sayi na wani, to an canza wancan tsari tun zamanin mulkin malaka wanda yake ma'adananku ne, amma wasu ne ke amfana.

Karuwar zuba jari a tattalin arzikin Najeriyar dai na zama abinda ke haifar da kyakyawar fata ga makomar kasar da ke da zarattan matasan da suka kosa domin samun ayyukan yi domin zaburara da tattalin arzikin kasar.

Mawallafi: Uwais Abubakar Idris

Edita: Usman Shehu Usman

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani