1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An nemi sanya wa sojoji takunkumi

Ramatu Garba Baba
August 5, 2019

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci kasashen duniya da su saka wa kasar Myanmar takunkumi sakamakon yadda  sojojin kasar ke musguna wa 'yan kabilar Rohingya

https://p.dw.com/p/3NO6M
Myanmar Proteste Armee Intervention Archivbild August 1988
Hoto: ullstein bild-Heritage Images/Alain Evrard

Tawagar majalisar da ke gudanar da bincike kan rikicin kabilancin da ya haifar da kisan kiyashi, ta ce ta gano yadda rundunar ke amfani da kafar wajen samun kudin siyan makamai da zummar shafe 'yan kabilar Rohingya daga doron kasa.

'Yan kabilar Rohingya fiye da dubu dari bakwai ne dai, suka tserewa rikicin kasar zuwa Bangladesh a shekarar 2017. Majalisar Dinkin Duniya da sauran kasashen Turai sun ce an aikata kisan kiyashi da yi wa mata fyade a yayin rikicin inda ta dora alhakin kan sojojin gwamnati, lamarin da aka ce ya sabawa dokokin kasa da kasa. Tun bayan fidda sakamakon, gwamnatin Myanmar ba ta ce kalla ba kan wannan zargin.