1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaPapua New Guinea

Mutanen da kasa ta binne a Papua New Guinea sun haura 2,000

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
May 27, 2024

Faruwar ibtila'in ta sabbaba rushewar gidaje da lalacewar hanyoyi da gonaki

https://p.dw.com/p/4gJay
Hoto: Mohamud Omer/International Organization for Migration/AP/picture alliance

Kasar Papua New Guinea ta sanar da Majalisar Dinkin Duniya cewa mutanen da kasa ta binne sun haura 2,000, biyo bayan zaftarewar kasar da ta haddasa bajewar tsaunin Mugalo, a lardin Enga mai tsaunuka a makon da ya gabata.

Karin bayani:Yarjejeniyar tsaro

Faruwar ibtila'in ta sabbaba rushewar gidaje da lalacewar hanyoyi da gonaki, lamarin da ya jefa al'umma cikin mayuwacin hali, sakamakon kangin rayuwa da suka shiga.

Karin bayani:Sojoji na yin bore a Papua New Guinea

Cikin wani sako da ta aikewa Majalisar Dinkin Duniya, Papua New Guinea ta nemi agajinta da ma sauran kasashen duniya, don ceto ta daga mawuyacin halin da ta samu kanta a ciki,bayan mutuwar mutane 670.

Tuni dai kasar Australia ta alkawarta agazawa kasar, kamar yadda mataimakin firaministan kasar Richard Marles ya sanar.