Mutane tara sun mutu a bukukuwan Sallah a Ghana
July 7, 2016Talla
Mutane tara ne suka mutu da yammacin ranar Laraba a wani filin taro na Asawase da ke karkashin majalisar karamar hukumar Asokore Mampong da ke birnin Kumasi na kasar Ghana, sakamakon ture-ture da aka fuskanta a lokacin da ake gudanar da shagulgulan karamar Sallah ta karshen Azumin watan Ramadan.
Da yake magana kan wannan hargitsi da ya faru, Nurudeen Hamidan da ke a matsayin shugaban karamar hukumar, ya tabbatar da mutuwar mutanen tara, maza shida da mata uku, dukkansu yara matasa. Ga al'ada dai matasa maza da mata dai ne ke haduwa a wannan fili a duk karshen watan Azumin Ramadan domin gudanar da shagulgulan Sallah.