1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Habasha: Mutane 67 sun mutu a zanga-zanga

Binta Aliyu Zurmi
October 25, 2019

A kasar Habasha zanga zangar adawa da Firaminista Abiy Ahmed wadda ta rikide zuwa rikicin kabilanci a yankin Oromiya ta haddasa hasarar rayukan mutane 67.

https://p.dw.com/p/3Ry5T
Unterstützer von Jawar Mohammed versammeln sich in Addis Abeba
Hoto: AFP/Stringer

Shugaban 'yan sanda na yankin Oromiya Kefyalew Tefera ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa daga cikin mutanen 67 da suka rasu 55 fararen hula ne yayin da ragowar kuma jami'an tsaro ne. 

Takaddama ta kunno kai a kasar ta Habasha sakamakon rashin jituwa tsakanin Firaminista Abiy Ahmed da tsohon na hannun damansa Jawar Mohammed da suka yi hannun riga da kuma rashin gamsuwa da wasu mutanen Oromiya suke nunawa game da salon mulkin gwamnatin Abiy Ahmed wanda shima dan yankin Oromiya ne. 

Sabon rikicin dai na iya jefar kasar ta Habasha wadda ke fama da rigingimun kabilanci cikin wani wadi na tsaka mai wuya.