1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane 17 suka mutu a gobarar Landan

Abdourahamane Hassane
June 15, 2017

Masu aikin ceto a birnin Landan na can na ci gaba da kokarin nemam mutane da suka yi batan dabo, a cikin benen da ya yi gobara a daran Larba.

https://p.dw.com/p/2ekx7
UK Mindestens zwölf Tote und dutzende Verletzte bei Hochhausbrand in London
Hoto: Reuters/T. Melville

Shugaban jami'an aikin kwana-kwana na Landan Dany Cotton ya ce da wuya a samu wadanda ke da sauran shan ruwa a gaba a cikin yanayin da wutar take kara ruruwa ga kuma tsananin zafi. Wasu kafofin yada labarai sun ambato gomai na iyalai da suka bace wadanda har ya zuwa yanzu ba a ji duriyar su ba. Ko da shi ke ya zuwa yanzu ba  san dalilan tashin gobarar ba, amma dai ,jama'ar da ke zaune a soron  benen na yn korafin a game da rashin tsari wajen tafiyar da ayyuka samar da lantarki a benen.