1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwango: Hadarin jiragen kasa ya halaka mutane 13

July 1, 2019

Kimanin mutane 13 suka halaka sakamakon hadarin jiragen kasa a yankin kudancin kasar Jamhuriyar Dimukudiyyar Kwango.

https://p.dw.com/p/3LQCG
Südafrika Zugunglück
Hoto: picture-alliance/AP Photo


A Jamhuriyar Dimukudiyar Kongo mutane 13 sun gamu da ajalinsu sakamakon wani hadarin jiragen kasa da ya auku a daren Lahadi wayewar wannan Litinin. Hadarin ya auku ne a kusa da Pointe-Noire da ke kudancin kasar bayan da  jiragen kasar 2 shake da kaya sukayi karo da junansu.

Majiyoyi daga cibiyar kula da zirga-zirgar jaragen kasa cewa da CFCO su labarta cewa daya daga jiragen ya samu matsalar naura ne lamarin da ya kai shi yin cikin daya jirgin dake kan hanyar sa. Hukumar 'yan sandar Kongo ta tabbatar da aukuwar hadarin wanda ya lakume rayukan mutane 13 wadanda galibi pasinjoji ne.

Ba bakon abu ne ba dai samun hadarin jiragen kasa a wannan yanki na Jamhuriyar Dimukudiyyar Kwango domin ko da a shekarar 2010 wani hadari makamancin wannan ya ristsa da rayukan mutane fiye da 50.