1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Musayar harbe-harbe a gabashin Kongo

August 27, 2013

'Yan tawayen M23 sun sake buɗe wuta a kan dakarun Kongo da ke samun tallafin ƙasashen duniya.

https://p.dw.com/p/19XcT
A child stands in front of Indian soldiers of the UN mission in the Democratic Republic of Congo (MONUSCO) driving an armoured vehicle at the border zone in Kagnaruchinya, 7 km north of Goma, on June 2, 2013. The M23 rebellion -- launched by Tutsi former soldiers who mutinied in April 2012 -- is the latest in years of violence that have ravaged the vast central African country's mineral-rich east. A peace deal signed in February by 11 regional countries had brought relative calm until it was broken in the three days leading up to Ban's visit. The two sides stopped fighting while the UN leader toured the flashpoint city of Goma. AFP PHOTO/Junior D. Kannah (Photo credit should read Junior D. Kannah/AFP/Getty Images) Erstellt am: 02 Jun 2013
Hoto: Junior D. Kannah/AFP/Getty Images

'Yan tawayen M23 sun sake ƙaddamar da hare-hare a kan dakarun Kongo, da ke wajen garin Goma, a yankin gabashin ƙasar. A cewar Olivier Hamuli, kakakin rundunar soji a yankin arewacin Kivu, tun a wannan Litinin ce,ɓangarorin biyu suka fara musayar wuta a yankin Kibati, mai tazarar kilomita 20 daga arewacin garin Goma, da ke zama babban birnin lardin arewacin Kivu. Jami'in sojin ya fadi ta tashar rediyon Okapi, da ke ƙasar cewar, a shirye sojojin suke su ɗauki fansa a duk lokacin da 'yan tawayen suka yi yunƙurin nausawa gaba. Tun a ranar Larabar da ta gabata ce, dakarun Kongo, waɗanda ke samun tallafin rundunar kiyaye zaman lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya a Kongo, ke fafatawa da 'yan tawayen M23, waɗanda ke sabunta hare-haren da suke kai wa.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Abdourahamane Hassane