Mugabe ya sallami mataimakiyarsa
December 9, 2014Talla
Shugaba Mugabe na Zimbabwe ya sallami mataimakiyarsa Joice Mujuru, kwanaki bayan da ta rasa kujerarta a jam'iyya mai mulki, kuma ana sa ran zai bayyana majalisar zartarwarsa a yau Talata kamar yadda wasu mijiyoyi biyu na gwamnatin suka bayyana wa kamfanin dillancin labaran Reuters.
Majiyoyin da basu so a bayyanasu ba, saboda a cewarsu ba a basu ikon magana ba da manema labarai ba, Majuru ta karbi takardar sallamarta a daren jiya Litinin makonni bayan da ake zirginta da kitsa wani shiri na kawar da gwamnatin ta shugaba Mugabe.
Mawallafi: Yusuf Bala
Edita: Umaru Aliyu