Moroko ta yi barazanar zuwa kotu
July 22, 2021Talla
A tsakiyar wannan makon ne dai wani rukunin masu bincike suka bankado cewa an yi amfani da manhaja mallakar wani kamfani mai suna NSO na Isra'ila, wajen sauraren wayoyin dumbin jama'a da suka hada da 'yan siyasa da 'yan jarida da masu fafatukar kare hakkin bil Adama da ma wasu jami'an gwamnati ciki har da Shugaban Faransa Emmanuel Macron.
Gwamnatin Morokon dai ta karyata wannan batun tana mai cewar za ta gudanar da bincike a kai.