1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yanci da walwalar jama'a na gamuwa da cikas a duniya

Abdourahamane Hassane
February 25, 2019

An bude taro shekara-shekara na MDD a kan sha'anin kare hakin bil Adama karo na 40 a Geneva, wanda a taron babban sakataran MDD António Guterre ya ce duniya na fuskantar barazana.

https://p.dw.com/p/3E5LW
Antonio Guterres babban sakataran MDD
Antonio Guterres babban sakataran MDDHoto: picture-alliance/KEYSTONE/S. Di Nolfi

A lokacin da yake jawabi a wajen taron sakataran MDD António Guterre ya yi kiran da a kawo karshen wariyar jinsi da rashin juriya kuma ya ce da sannu a hankali 'yancin dan Adam na samun koma baya a kasashen duniya da dama. Kana ya yi Allah wadai da karuwar 'yan mulkin populiste abin da ya ce hadari ne da kuma  ci gaba da yada jawaban kiyaya a kafofin sada zumunta.