1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mayakan Tigray sun yi watsi da rahotannin tada hankali

Abdul-raheem Hassan
November 7, 2021

'Yan tawayen da ke yaki da gwamnatin Habasha sun yi watsi da rahotannin cewa za su haifar da "zubar da jini" idan suka shiga birnin Adis Ababa, duk da cewa dubban mutane sun yi gangamin marawa sojoji baya a Addis Ababa.

https://p.dw.com/p/42h1W
Ätopien | Unterstützer des Premierministers feiern
Hoto: Tiksa Negeri/REUTERS

Mayakan kabilar Tigrai (TPLF) da kawayensu sun shafe shekara guda suna gwabza yaki da gwamnatin Ethiopia, wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da jefa wasu da dama cikin mawuyacin hali.

Firaiminista Abiy Ahmed, wanda ya lashe kyautar Nobel ta zaman lafiya ta 2019, ya tura sojoji cikin yankin Tigray a watan Nuwambar 2020 don kawar da kungiyar ta TPLF kan zarginsu da kai hari kan sansanonin soji.

Sai dai kungiyar ta TPLF da kawayenta, ta sha ikirarin samun nasarori da dama a cikin 'yan makonnin da suka gabata, inda suka yi ikirarin kwace garuruwa masu tazarar kilomita 400 daga babban birnin kasar.