1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matsalar tsaro a Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya

November 26, 2013

Faransa ta bayyana kyakkyawan kudirin tallafawa kokarin da Majalisar Dinkin Duniya ke yi na daidaita tsaro a Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya.

https://p.dw.com/p/1AOwd
A French soldier of the BOALI operation in Central African Republic checks a car at a checkpoint near Bangui Airport on October 10, 2013. The Central African Republic has been shaken by a recent increase in clashes between ex-rebels of the Muslim Seleka coalition that led the coup and local self-defense groups formed by rural Christian residents, the religoin of around 80 percent of the population. The poor but mineral-rich nation was plunged into chaos when a coalition of rebels and armed movements ousted longtime president Bozize and took the capital Bangui in March. AFP PHOTO / ISSOUF SANOGO (Photo credit should read ISSOUF SANOGO/AFP/Getty Images)
Hoto: ISSOUF SANOGO/AFP/Getty Images

Kasar Faransa ta bayyana cewar, za ta aike da dakaru dubu daya zuwa Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya, a karkashin rundunar da Majalisar Dinkin Duniya za ta tura domin samar da zaman lafiya a kasar, wadda ke ci gaba da fuskantar rigingimu.

Ministan tsaron Faransa, Jean-Yves Le Drian, shi ne ya sanar da hakan, yini daya kachal bayan da wani babban jami'in Majalisar Dinkin Duniya ya yi kashedi game da yuwuwar kissan kiyashi, da kuma barkewar yakin basasa a kasar, wadda ke zama daya daga cikin kasashen da suka fi fama da talauci a duniya, wadda kuma ke ci gaba da fama da rigingimu, tun bayan da 'yan tawayen kasar suka kifar da gwamnatin tsohon shugaban kasar, Farancoir Bozize a watan Maris.

Kungiyoyin kare hakkin jama'a dai na zargin 'yan tawayen da laifukan da suka hada da kissan jama'a, da yi wa mata fyade, da kuma tilastawa kananan yara shiga cikin aikin soji. Dama dai kasar Faransa tana da dakarun da yawansu yakai 420 a Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya, galibinsu kuma, na bada kariya ne ga filin sauka da tashin jiragen sama na Bangui, babban birnin kasar.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Usman Shehu Usman