1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Rikici ya barke a tsakanin kungiyoyin ta'adda

Ramatu Garba Baba
September 7, 2022

Kazamin rikici ya barke a tsakanin wasu kungiyoyi masu gwagwarmaya da makamai a Mali inda Kungiyar IS ta yi nasarar kwace ikon garin Talataye daga hannun 'yan tawaye.

https://p.dw.com/p/4GXz1
Mali Tuareg Unabhängigkeitsbewegung Mouvement national de libération de l'Azawad MNLA
Hoto: AP

Rahotanni daga kasar Mali sun tabbatar da labarin rikicin da ya barke a tsakanin kungiyoyin 'yan ta'adda da ke gaba da juna, inda daga bisani Kungiyar IS ta yi nasarar kwace ikon garin Talataye da ke karkashin ikon 'yan tawayen Azawad na 'yan kabilar Touareg da suka yi kaka-gida a yankin arewacin kasar.

Wani jami'in tsaro na yankin da bai yarda a fadi sunansa ba, ya ce, an kwashi fiye da sa'oi uku ana gwabza fadan, amma kawo yanzu mahukuntan Malin ba su yi tsokaci kan fadan dama irin asarar da aka tafka ba. Kasar Mali ta shafe shekara da shekaru tana fama da munanan hare-haren mayakan jihadi da suka addabi kasashen yankin Sahel, musamman jamhuriyar Nijar da Burkina-Faso da ke makwabtaka da Malin.