Rikicin kabilanci ya lakume rayuka 95
June 11, 2019Talla
An zargi maharan da cinna wa kauyen wuta bayan da suka kashe mutanen a yayin harin. Majalisar Dinkin Duniya ta yi alla-wadai da harin da ya jefa kasar cikin yanayi na jimami, inda ta bukaci bangarorin da lamarin ya shafa da su guji kai hari irin na ramuwar gayya. Gwamnatin kasar ta sha lawashin gudanar da bincike don gano wadanda ke da hannu a wannan aika-aikan.
Ko a watan Maris na wannan shekarar, mutum dari da hamsin ne suka mutu bayan wani fada a tsakanin mafarauta da Fulani a kauyen na Dogon, harin da aka ce shi ne mafi muni a tarihin kasar ta Mali.