1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar dattawan Najeriya ta ce da sakel a yaƙi da ta'addanci

Usman ShehuMarch 21, 2013

Sanatocin Tarayyar Najeriya sun buƙaci shugaba Jonathan da ya sauya dabar amfani da ƙarfi bisa yaƙar ta'addanci a ƙasar, inda suka ce ɓarnan kuɗi ne kawai ba ci gaba

https://p.dw.com/p/182Iy
Titel: DW_Nigeria_Integration6 Schlagworte: Polizeihauptquartier, Anschlag Boko Haram, Abuja Fotograf: Katrin Gänsler Aufnahmedatum: 16. Juni 2011 Aufnahmeort: Abuja, Nigeria Bildbeschreibung: Anschlag der islamistischen Terrorgruppe Boko Haram auf das Polizeihauptquartier in Abuja
Wani harin bam da aka kai a AbujaHoto: Katrin Gänsler

A wani abun dake zaman kama hanyar gwada kwanji a tsakanin fadar gwamnatin kasar da yan majalisar Tarrayar a kan batun yakin da ta'addancin kasar dake cikin shekarar sa ta uku, majalisar dattawan kasar ta nemi sauyin taku a bangaren gwamnatin da ta bada kudi amma kuma wankin hula ke neman kai ta dare

An dai ga kisan dubban milliyoyin Nairori an kuma share dare da farmaki iri-iri, to sai dai kuma daga dukkan alamu tana shirin zaman an kasa ga gwamnatin da a karon farko ke fuskantar dawowa daga rakiyar gwamnatin kasar a cikin yakin da ta'adancin ta a bangaren majalisar dattawan kasar.

A picture taken on April 18, 2011 shows Nigerian police enforcing a curfew in the capital of Bauchi state, nothern Nigeria, after riots, run by muslim youth, broke out in Bauchi. Nigeria's Goodluck Jonathan has been declared winner of presidential elections in a landmark vote that exposed regional tensions and led to deadly rioting in the mainly Muslim north. Jonathan, the incumbent and first president from the southern oil-producing Niger Delta region, won 57 percent of the vote in Africa's most populous nation, easily beating his northern rival, ex-military ruler Muhammadu Buhari. AFP PHOTO / Tony KARUMBA (Photo credit should read TONY KARUMBA/AFP/Getty Images)
Rundunar yan sandan NajeriyaHoto: Getty Images/AFP

Majalisar dattawan kasar dai tace lokaci ya yi na mantawa da batun karfin tuwo da nufin kawo karshen matsalar dake cikin shekarar ta ta uku da kuma ta kai ga lamushe rayukan yan kasar da dama.

Yan majalisar da suka zauna suka yi nazari da karatu irin na ta natsu dai, sun ce daga hakarkari da na isa kan batun karfin tuwo ga yakin dai batu ne da ya kamaci zama tarihi a bangaren mahukuntan kasar da suka zauna suka kalli karuwar tashin boma bomai ba adadi a cikin dan kankanin lokaci.

Sabon martanin majalisar da ya zo kasa da yan kwanaki da harin da ya hallaka mutane da dama a birnin Kanon Dabo, sannan kuma ya sake tada tsohon mikin matsalar dai daga dukkan alamu na iya bude sabon babin rikici a tsakanin fadar gwamnatin da shugaban ta yace basu da niyyar yin ahuwa ga fatalwa da kuma yan majlisar da suke cewar karatun nasa bai zo daidai da tunani irin na shugabanni ba. Abun kuma da a cewar Senator Kabiru Gaya dake zaman dan majalisar dattawa daga jihar Kano ya sanya sauko wa daga dokin nakin zama wajibi.

A man stands in front of some burnt buses at a motor park in Sabon Gari, after Monday's explosions in Kano March 19, 2013. Five explosions at a bus park in northern Nigeria's main city of Kano killed at least 25 people on Monday, a Reuters witness said, in an area where Islamist sect Boko Haram is waging an insurgency against the government. The coordinated bombing came as an audio tape emerged of a man saying he was the father of a family of seven French tourists kidnapped by Boko Haram militants. REUTERS/Stringer (NIGERIA - Tags: CIVIL UNREST POLITICS)
Harin da aka kai wa wasu motocin Safa a KanoHoto: Reuters

Zaman lafiya a cikin kasa ko kuma ci gaba a cikin asarar rayuka dai, ko bayan matsin lambar cikin gidan kasar ta Najeriya dai, gwamantin har ila yau na fuskantar sabuwar annobar satar baki yan kasashen wajen da daga dukkan alamu ta kama hanyar kara jefa fadar ta Aso Rock cikin tsaka mai wuya.

Shugaban kasar ta Najeriya dai alal misali ya share tsawon mako na jiya yana bada tabbaci na kariya dama ceto bakin a idanun shugabannin dake kai kawo cikin kasar da nufin neman mafitar matsalar.

epa03095737 Nigerian boys sift through the remains of the Gamboru market after multiple explosions in Maiduguri, northern Nigeria, 07 February 2012. Three people have died in bomb blasts by the radical Islamist group Boko Haram in northern Nigeria, police said 07 February. Police told the German news agengy dpa that the owner of a pharmacy in the northeastern city of Maiduguri, and two of his employees, were killed when bombs went off. In the city of Kano, two police stations where Boko Haram members were being detained were also targeted. Police said there were no deaths. Boko Haram claimed responsibility for both attacks, which occurred as residents were observing Eid-el-Mulud, the Muslim festival marking the birth of the Prophet Mohammed. In the nearby town of Kaduna a man in military uniform was reported to have blew himself up outside an army barracks. Boko Haram Islamist militants have recently killed hundreds in bomb attacks across northern Nigeria. EPA/STR
Harin bam da aka kai a kasuwar MaiduguriHoto: picture-alliance/dpa

To sai dai kuma a cewar Dr Doyin Okupe dake zaman mashawarcin shugaban kan harkokin jama'a duk wani kokari na kushe gwamnatin na zaman batu na rashin sanin al'amura.

"Wadanda suke irin wadannan kalamai basu da masaniyar abun da ake nufi da yaki da ta'addanci cikin kasa. Matsala ce babba musamman ma inda yan ta'addan ke zaman na cikin gida kamar Boko Haram".

Abun jira a gani dai na zaman mataki na gaba cikin rikicin da ya fyadi sarki sannan kuma ya kai ga rauni ga ruhi dama arzikin talakan cikin kasar ta Najeriya.

Mawallafi: Ubale Musa

Edita: Usman Shehu Usman