Al'umma a Jihar Zamfara na cikin fargaba
September 13, 2018Talla
Rundunar yan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da afkuwar lamarin a ta bakin kakakin ta SP Shehu Muhammad. Wakilin DW a Zamfara Yusuf Ibrahim Jargaba, ya bayyana cewa kakakin 'yan sandan ya kara da cewar jami'an tsaro ba su yi kasa a gwiwa ba, suna samun labarin harin suka garzaya yankin da lamarin ya faru, ya kuma jaddada alwashin rundunar na ganin an gano wadanda suka aikata wannan hari, don su girbi abinda suka shuka.