1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa ya bukaci adalci a rabon yan cirani

Zulaiha Abubakar
September 19, 2019

Shugaban Faransa Emmanuel Macron da Firaministan Italiya Giuseppe Conte sun bukaci Kungiyar Tarayyar Turai ta bullo da sabon tsarin rabon 'yan gudun hijira a tsakanin kasashen nahiyar.

https://p.dw.com/p/3PqzD
Italien: Giuseppe Conte und Emmanuel Macron in Rom
Hoto: picture-alliance/dpa/R. De Luca

Shugaban Faransa Emmanuel Macron da Firaministan Italiya  Giuseppe Conte sun yi wannan kiran ne a ranar Laraba yayin da suke kokarin sasantawa kan tsamin dangantakar da aka samu a tsakanin kasashen biyu a karkashin gwamnatin Italiya da ta gabata mai akidar kyamar baki.

Kasar Italiya dai ta sha yin korafi cewa sauran kasashen Turai ba sa daukar nauyin da ya dace na dubban daruruwan 'yan gudun hijira da suka isa gabar ruwan Italiya a 'yan shekarun baya bayan nan.