1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Macron da Guelleh sun magantu kan Habasha

Abdoulaye Mamane Amadou
September 11, 2022

A yayin da rikici ke kara rintsabewa tsakanin gwamnati da 'yan tawaye a Habasha, shugaban Faransa Emmanuel Macron ya tattauna ta waya da takwaransa na Jibuti Ismaïl Omar Guelleh.

https://p.dw.com/p/4Ggdq
EU-Gipfel in Brüssel
Hoto: Olivier Matthys/AP Photo/picture alliance

Shugaba Emmanuel Macron ya ce kasarsa na cike da zumudin ganin samun dawamammen zaman lafiya a Jibuti da ma yankin Kahon Afirka baki daya, a yayin tattaunawarsu ta war tarho da shugaba Ismaïl Omar Guelleh.

Fadar Elysée ta ce burinta a samu kwanciyar hankali a karamar kasar duba da yadda tashe-tashen hankula ke kara kamari tsakanin gwamanati da dakarun 'yan aware da ke a makwabciyar kasar Habasha, lamarin da ke kara haifar da fargaba da karancin cimaka.

Faransa ta jibge dakarun sojinta akalla 1.500 a Djibouti a wani sansanin na musamman da ke zaman ko takwana.