1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jam'iyyun adawar Libiya sun amince da ranar zabe

Zulaiha Abubakar
May 29, 2018

Jam'iyyun adawar Libiya sun amince da zaben shugaban kasa tare da na 'yan majalisun dokokin kasar a ranar goma ga watan Disambar wannan shekarar yayin wani babban taro a birnin Paris.

https://p.dw.com/p/2yX53
DW Conflict Zone Taher El-Sonni
Hoto: DW/A. MacKenzie

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ne ya gayyaci jagororin jam'iyyun hamayyar na Libya don nemo hanyoyin da za a kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru bakwai ana yi a kasar. Tun da fari babban mai ba gwamnatin kasar Libya shawara Taher al-Sonni ya rubuta a shafinsa na Twitter cewar bangarorin jam'iyyun hudun sun cimma matsaya kan kammala tsarin mulkin kasar ta Libya don gudanar da zabe a watan Disamba.