1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boren kin jinin gwamnati na kara zafi a Lebanon

Abdoulaye Mamane Amadou
December 16, 2019

Arangama ta sake barkewa tsakanin masu zanga-zangar kin jinin gwamnati da jami'an tsaro a babban birnin kasar Lebanon, tare da zama musabbabbi na raunata mutane da dama.

https://p.dw.com/p/3UsJ7
Libanon Erneut Zusammenstöße zwischen Demonstranten und Sicherheitskräften in Beirut
Hoto: Reuters/I. Abdallah

Rahotanni sun ce masu boren sun jefa kwalaben ruwa da sauran ababen jifa ga jami'an tsaron, lamarin da ya harzuka su inda suka yi amfani da mesa da hayaki mai sa kwalla domin tarwatsa masu boren. 
Wannan lamarin na zuwa ne 'yan awowi kalilan bayan da jami'an tsaro sun yi amfani da harsasan roba wajen tarwatsa masu zanga-zanagar lamarin da ya rauwanata akalla mutane 36.

Tun a ranar 17 ga watan Oktoban wannan shekarar ne dai bore da kin jinin gwamnati suka barke a kasar ta Lebanon tare da zama musabbabin marabus din Firaminista Saad Hariri, to amma sai dai tun sdaga lokacin kawo yanzu majalisar dokokin kasar ta kasa samun wani sabon firaministan da zai karbi jan ragamar gwamnatin kasar.