1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kwashe jami'an tsaro saboda barazanar tsaro

Ramatu Garba Baba
November 26, 2019

Hukumar Lafiya ta Duniya ta kwashe jami'an da ke aikin riga-kafin cutar Ebola daga yankin Beni na jamhuriyyar Dimokradiyar Kwango a sakamakon barazanar tsaro da suke fuskanta.

https://p.dw.com/p/3Tkt6
Demokratische Republik Kongo l anhaltende Ebola-Epidemie
Hoto: picture alliance/AP Photo/J. Delay

Hukumar Lafiya ta Duniya wato WHO ta ce, ta kwashe ma'aikatanta da ke aikin bayar da riga-kafin cutar Ebola a yankin Beni na Jamhuriyyar Dimokradiyar Kwango bayan da aka fuskanci barazanar da rayuwarsu ke ciki na tsaro. An gaggauta amfani da wani karamin  jirgin sama a aikin kwashe ma'aikatan su 49 daga garin zuwa birnin Goma ne daren jiya Litinin. 

Hukumar dai ta yi gargadin halin da za a sami kai ciki, muddun matsalar tsaro ta ci gaba da haifar da tsaiko ga aikin dakile cutar mai saurin kisa, inda ta nemi a yi hattara.

Yankin na Beni na daya daga cikin yankunan Jamhuriyyar Kwango da ke fama da tsananin rashin tsaro amma kuma ke fama da annobar cutar Ebola. A baya-bayan nan, fararen hula kusan saba'in da bakwai aka kashe a wani hari da aka kai a  farkon wannan watan na Nuwamba. An kiyasta cewa, cutar ta Ebola ta lakume rayukan mutum sama da dubu biyu.