1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yunkurin kawo karshen matsalar tsaro a Kwango

Abdoulaye Mamane Amadou
September 22, 2022

Shugabanin Rwanda da Jamhuriyar Dimukaradiyyar Kwango sun tattauna batun hanyoyin magnce zubar da jini da ake fuskanta a yankunan gabashin Kwango da yayi sanadin mutuwar fararen hula.

https://p.dw.com/p/4HBCT
USA UN Generalversammlung in NY l Rede des kongolesischen Präsidenten Tshisekedi
Hoto: Angela Weiss/AFP

Fadar Elysée ta birnin Paris ta ce Shugaba Kagame na Ruwanda da takwaransa Félix Tshisekedi na kasar Kwango sun yi tattaunawar keke da keke karkashin jagorancin Shugaba Emmanuel Macron na Faransa, kana shugabannin biyu sun kama hanyar sulhunta rikicinsu da batun samar da zaman lafiyar da ya buwa a yankin gabashin Kwango, yankin da kungiyar M23 mai tada kayar baya ke cin karenta ba babbaka.

Bayan M23 kasashen biyu, sun kuma bayyana anniyarsu ta tunkarar barazanar tsaron da kungiyar ADF mai ikrarin jihadi a yankuna da dama na Jamhuriyar Dimkuradiyyar Kwango ke yi a yayin taronsu na su a birnin New York.