1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwango da M23 sun watse baram-baram

Carl Richard HolmNovember 12, 2013

Gwamnatin Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kwango da 'yan tawayen ƙasar wato M23 sun gaza cimma yarjejeniyar zaman lafiya tsakaninsu a zaman da suka yi a Yuganda.

https://p.dw.com/p/1AFfO
Congolese soldiers rest while being deployed against the M23 rebels near Bunagana, north of Goma, November 1, 2013. Uganda called on the Congolese army and M23 rebels to cease fire on Friday as peace talks progressed in Kampala to end their 20-month conflict. While the rebels said they were ready for a peace deal, government forces vowed to pursue their military advantage and crush the rebellion in the Democratic Republic of Congo's mineral-rich east. REUTERS/Kenny Katombe (DEMOCRATIC REPUBLIC OF CONGO - Tags: MILITARY CIVIL UNREST)
Hoto: Reuters/Kenny Katombe

Gwamnatin Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kwango da kuma Ƙungiyar tawaye ta M23 sun ɗage lokacin da za su rattaɓa hannu a kan yarjejeniyar zaman lafiya bayan da hukumomin Kinshasa suka buƙaci ƙarin lokacin domin yin nazari. Da farko dai jami'an dipolomasiya na ƙasashen Turai da kuma manyan jami'an gwamnatin Yuganda sun yi fatan ganin sassa biyu sun sa hannu a kan wannan yarjejniya shekara guda bayan fara zaman tattaunawa.

Kakakin gwamnatin Yuganda ya bayyana cewar an samu rashin fahimta daga ɓangaren gwamnatin Kwango game da suna ko taken da ya kamata a bai wa wannan yarjejeniya. Har yanzu dai ba a san lokacin da ɓangarorin biyu za su sake zama don rattaɓa hannu a kan yarjejeniyar zaman lafiyar ba. Da ma ana ganin cewar ita ce za ta iya kawo ƙarshen rikicin da yankin gabashin Kwango ya shafe shekaru ya na fama da shi.Tun dai kwanakin da suka gabata ne dakarun gwamnati suka yi ta samun nasara a kan 'yan tawaye inda suka yi nasarar fatattakarsu daga gabashin ƙasar ta Kwango.

Mawallafi: Mouhamadou Awal Balarabe
Edita: Abdourahamane Hassane