1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaman zullumi kan zaben Dimukuradiyyar Kwango

Suleiman Babayo AS
January 5, 2019

Hukumar zaben Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango ta jinkirta bayyana sakamakon zabe da aka yi a kasar inda ta ce sai nan da mako guda ne za ta fidda shi, batun da ya haifar da zaman zullumi a kasar.

https://p.dw.com/p/3B4m0
DR Kongo nach der Wahl
Hoto: Reuters/B. Ratner

Hukumar zaben kasar Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango ta jinkirta sakamakon zaben da ta niyyar sanarwa gobe Lahadi, inda ta kara mako guda kamar yadda shugaban hukumar Corneille Nangaa ya tabbatar. Nangaa ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa suna kokari amma tilas su kara mako guda.

Hakan ya zo ne daidai lokacin Cocin Katolika na kasar ke gargadin hukumar zaben ta fitar da sakamakon na zahiri maimakon sauya abin da mutane suka zaba.

Zaman zulumin da ake yi a kasar ta Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango yayin da ake jiran sakamakon zabe ya sanya Shugaba Donald Trump na Amirka turo sojojin 80 zuwa kasar Gabon domin kare ofishin jakancin Amirka a Kwango din inda aka samu wata hatsaniya.