SiyasaAfirka
Kotu ta saki Sowore bisa wasu ka'i'doji
January 11, 2021Talla
Tun a jajiberen shiga sabuwar shekarar nan ne dai aka kame Sowere da mutane hudu kan zargin taro ba bisa doka ba, da kitsa yunkurin tunzura jama’a, zargin da ya musanta. Comrade Bako Abdul shugaban kungiyar Campaign for Democracy ya ce belin da aka ba Sowore ya nuna cewa Najeriya ta fara inganta tsarinta na dimukuradiyya.
Wakilin DW a Abuja Uwais Abubakar Idris ya ce kotun majistare ta sanya ka'idar cewa Mr. Sowere ba zai bar Abuja ba, kuma dole ne a ranakun Litinin da Jumma’a ya kai kansa kotu ko da ba za a yi zaman shari’a ba har zuwa lokacin da za a kamala shari'ar.