Kotu ta tuhumi tsohon shugaban Chadi
July 2, 2013Talla
Da yake yinn tsokaci a kan tuhumar lauyan da ke kare tsohon shugaban Maitre Diouf ya ce :'' Habre na fuskantar wani al' amari ne, na sace shi da aka yi, kana aka yi garkuwa da shi, wanda kuma ya ce muke ɗora alhakin haka a kan wasu sojojin.''
Hissene Habre ɗan shekaru 71 a duniya na zaune a ƙasar ta Senegal tun a shekara ta 1990 lokacin da gwamnatinsa ta faɗi. Nan gaba ne dai kotun ta musammun da aka kafa za ta yi masa shari'a, a kan zargin da ake yi masa na aikAta kisa a kan mutane kusan dubu 40 waɗanda wasunsu suka mutu a gidajen kurkuku.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe