1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu a Najeriya na tuhumar Mustapha Umar

July 2, 2013

Babbar kotu da ke Abuja ta yanke hukuncin cewa mutumin da ake zargi da kai harin bom domin tarwatsa ofisoshin jaridun This Day da Moment yana da laifi.

https://p.dw.com/p/190IW
epa03197102 Security officials gather at the site of a bomb blast at 'This Day' Newspaper office in Abuja, Nigeria, 26 April 2012. Newspaper offices in two Nigerian cities were targeted in coordinated bomb blasts, with several casualties reported, the authorities said. The offices of This Day newspaper in the capital Abuja and Kaduna city were attacked. At least one person was killed and many more were injured, officials said. Rescue workers gave conflicting accounts. Some said a suicide bomber blew up the newspaper's building in Abuja, while others said a bomb was planted at the office. The offices of newspapers Sun and Moment in Kaduna, north-central Nigeria, were also targeted in separate blasts. Four people are feared dead in those blasts and dozens injured, the authorities said. EPA/GEORGE ESIRI
Hoto: picture-alliance/dpa

Da ya ke yanke hukuncin mai shari'a Adeniyi Ademola ya bayyana cewa kotu ba ta gamsu da dalilan da wanda ake tuhuma ya gabatar ba, don haka ya zama wajibi ya fuskanci shari'a domin kare kansa.

Barrister Nurudeen Sulaiman shi ne lauyan da ke kare wanda ake tuhuma: Ya ce  '' babu allaƙa tsakanin laifin da aka aikata da wanda ake tuhuma da aikata laifin, don haka daga shaidun da suke a gaban kotu da waɗanda ya bayar har da ma waɗanda suka ba da shaida muna da ƙwarin gwiwa ɗari bisa ɗari cewa mune za mu samu nasara a shari'ar.''  A ranar 26 ga watan Afrilun 2012 ne yan sanda suka cafke Mustapha Umar jim kaɗan bayan mumunan harin bom da aka kai a ofisoshin jaridar da ke Kaduna. A yanzu an tsayar da ranar 30 ga watan Satumba domin ci gaba da wannan shari'a da za a kai ga lokacin da za'a yanke hukunci.

Mawallafi  : Abdourahamane Hassane
Edita        : Zainab Mohammed Abubakar