Mahara sun hallaka fararen hula 38 a kasar Mali
June 19, 2019Talla
Akalla mutane 38 ne suka hallaka a wani harin da wasu masu dauke da makamai suka kai wa wasu garuruwa biyu na 'yan kabilar Dogon da ke kasar Mali kusa da iyakar kasar da Burkina Faso.
Gwamnatin kasar ta Mali ta tabbatar da faruwar labarin a kauyukan Gangafani da Yoro, tare da bayyana cewar tana daukar matakin tsaro ta hanyar tura karin jami'an tsaro inda tuni suka soma sintiri a yankin, sai dai babban alkalin alkalan kasar da ke jagorantar wata cibiyar da ke yaki da ta'adanci ya ce adadin mutanen da suka mutu 14 ne kawai.
Ko a ranar tara ga watannan watan na Yuni wasu masu dauke da makamai sun kai farmaki a wani kauyen na 'yan kabilar Dogon tare da hallaka mutane 35 galibinsu mata da kanana yara.