1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kim da Trump sun kama hanyar fahimtar juna

Yusuf Bala Nayaya
February 28, 2019

Shugaba Donald Trump na Amirka da takwaransa na Koriya ta Arewa Kim Jong Un sun bayyana shirin samar da ofisoshin tuntuba a kasashen juna. Matakin da ke nuna alamar samun fahimta tsakanin kasashen biyu.

https://p.dw.com/p/3EEJp
Hanoi, US-Präsident Donald Trump trifft den nordkoreanischen Staatschef Kim Jong Un
Kim Jong Un
Hoto: picture-alliance/E. Vucci

Shugaba Kim dai na Koriya ta Arewa ya yi na'am da wannan bukata ta samar da ofishin tuntuba lokacin da yake bayani ana fassarawa yayin taron manema labarai a birnin Hanoi. Trump ya kara da cewa wannan mataki ne da zai kara matso da kasashen biyu su fara tafiyar da harkoki tare a hukumance. Kuma babbar nasara ce a cewar Trump.

Babban burin tattaunawar ta birnin Hanoi na Vietnam dai na zama dorawa a matakai na ganin an kai ga gabar da za a hana kasar ta Koriya ta Arewa mallakar makamai na nukiliya, ganin yadda kasar ke zakewa a gwaje-gwajen makamai da ke barazana ga tsaron duniya, sai dai Shugaba Kim ya ce da ba shi da aniya ta wargaza shirin makaman nukiliyar da ba ma zai halarci taron na Hanoi ba.