Kashe-kashe a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
May 3, 2014Wasu mutane da ake dangantawa da 'yan kungiyar Seleka da kuma Fulani da ke yankin arewacin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, na ci gaba da kai hare-hare inda suka kashe akalla mutane 20, a cewar wata majiya ta sojan kasar.
Wani babban sojan Misca na Tarayyar Afirka da ke ayyukan tsaro a wannan kasa, ya shaida wa kanfanin dillancin labaran kasar Faransa AFP cewar, mutanen sun kai hari a wasu garuruwa akalla goma na Markounda da ke arewa, wanda ake ganin nan gaba adadin wadanda aka kashen zai iya karuwa, ganin yadda ba'a dakatar da hare-haren ba.
Al'ummar garin Markounda dai ta watse ta bar garin yayin da wasu suka fantsama cikin dazuka, inda kawo yanzu aka tura dakarun Misca ya zuwa garin Paoua a birnin da ke makwabtaka da birnin na Markounda, inda nan ma ake kai harin. Ana zargin 'yan tsofufuwar kungiyar ta Seleka da tafka ta'asa a wannan yankin.
Mawallafi: Boukari Salissou
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe