1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar kasashen G5 na nema kara hada kai

Abdourahamane Hassane
December 15, 2019

Shugabannin kasashen yankin Sahel na G5 na gudanar da taron a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar domin kara neman hadin kai tsakanin kasashen don yaki da ta'addanci.

https://p.dw.com/p/3Upwa
Symbolbild- Nigera - Militärübung
Hoto: picture-alliance/dpa/P. de Poulpiquet

Shugabannin na tattauna halin da kasashen yankin na Sahel suka samu kansu na hare-haren da suke fuskanta daga kungiyoyin 'yan ta'adda. Wannan taro  na musammun na zuwa ne  bayan hare-haren da IS ta kai a barakin soji na Inates da ke kan iyaka da Mali wanda a ciki sojojin Nijar 71 suka rasa rayukansu. Daman dai shugabannin na kungiyar G5 sun shirya yin taron na Yammai gabannin halarta gayatar da shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya yi musu a Pau domin tattauna batun tSaro a yankin wanda daga bisani aka dage saboda harin Inates.