Kungiyar kasashen G5 na nema kara hada kai
December 15, 2019Talla
Shugabannin na tattauna halin da kasashen yankin na Sahel suka samu kansu na hare-haren da suke fuskanta daga kungiyoyin 'yan ta'adda. Wannan taro na musammun na zuwa ne bayan hare-haren da IS ta kai a barakin soji na Inates da ke kan iyaka da Mali wanda a ciki sojojin Nijar 71 suka rasa rayukansu. Daman dai shugabannin na kungiyar G5 sun shirya yin taron na Yammai gabannin halarta gayatar da shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya yi musu a Pau domin tattauna batun tSaro a yankin wanda daga bisani aka dage saboda harin Inates.