1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon shirin SDGs ya samu amintar duniya

Suleiman Babayo/YBOctober 1, 2015

Kasashen duniya 193 suka amince da aiwatar da sabbin muradun 17 nan da shekara ta 2030.

https://p.dw.com/p/1GhNq
Obama beim Gipfel zu Terrorismus im Rahmen der UN-Vollversammlung
Mahalarta taron Majalisar Dinkin DuniyaHoto: AFP/Getty Images/Mandel Ngan

Shugabannin kasashen duniya da suka hallara a shelkwatar Majalisar Dinkin Duniya da ke birnin New York na kasar Amirka, sun amince da sabon shirin ci-gaba mai dorewa wanda ya maye gurbin muradin karni da aka aiwatar a shekaru 15 da suka gabata, inda sabon shirin shima za a aiwatar a tsukin shekaru 15 masu zuwa.

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel tana cikin shuganbannin kasashen duniya da a karshen mako suka amince da sabon shirin ci-gaba mai dorewa, wanda ke da muradu 17 da wasu abubuwa kimanin 169 da sabon shirin ya kunsa.

Jamus ta bada goyon baya

"An yi magana da yawa a kai, ba sai na kara bayani a kai ba. Abun shi ne aiwatar da jadawalin."!

Kanzlerin Angela Merkel UN Vollversammlung in New York
Shugabar gwamnatin Jamus Angela MerkelHoto: Reuters/M. Segar

Merkel ta kara da cewa wannan shiri ne da kasar Jamus ke bai wa mahimmanci, kuma wanda za a saka a gaba cikin shekaru masu zuwa.

Sabon shirin ci-gaba mai dorewar zai lashe makudan kudade wajen aiwatarwa a shekaru 15 masu zuwa kuma ya shafi kusan illahirin kasashen duniya. Kristalina Georgieva da ke zama kwamishiniyar kasafi da kula da al'uma ta kungiyar Tarayyar Turai ta nemi kasashen duniya su zage damtse kan aiwatar da sabon shirin:

Kasashen Turai na tare da shirin

"Muna bukatar masu bayar da kudaden tafiyarwa da masu aiwatarwa su tashi tsaye maimakon surutu kawai kan abin da ake bukata ba."

Shugabannin kasashen duniya sun nuna zummar ba da makuden kudaden aiwatar da sabon shirin daga nan tuwa shekara ta 2030, ciki har da Shugaba Xi Jinping na kasar China wanda ya yi alkawarin kudade masu yawa, kuma kasar ke kan gaba wajen yawan mutane tsakanin kasasheh duniya.

USA Xi Jinping und Hassan Rohani in New York
Shugaba Xi Jinping da Hassan Rohani a AmirkaHoto: Imago/Xinhua

Kasashen duniya 193 suka amince da aiwatar da sabbin muradun 17 nan da shekara ta 2030, yayin taro a zauren Majalisar Dinkin Duniya. Ana sa ran shirin ya rage gibin da ke tsakanin masu arziki da matalauta, da magance matsalar sauyin yanayi da wasu manyan kalubale da duniya ke fuskanta.