Jamus: 'Yan sanda sun kame wani mahari
March 11, 2023Talla
A birnin Karlsruhe da ke kudancin Jamus 'yan sanda sun kawo karshen yin garkuwa da mutane da aka shafe sa'o'i da dama ba tare da zubar da jini ba. A yammacin Juma'a, wata runduna ta musamman ta kai farmaki a wata kemus inda mutumin ya yi garkuwa da mutane sha daya. 'Yan sanda sun ce an kama wani matashi mai shekaru 20 da ake zargi. A cewar bayanan farko, babu wanda ya jikkata.