Rabuwar kan adawa kafin zaben Kwango
November 12, 2018Talla
Bayan da 'yan fafutika da dama suka gudanar da zanga-zanga Jean-Marc Kabund babban sakataren jam'iyyar ta UDPS ya bayyana cewa 'yan jam'iyyarsu tun daga tushe sun bukaci Felix Tshisekedi ya janye daga wannan yarjejeniya sun kuma bashi sa'oi 48 ya aikata haka.
Shugabannin 'yan adawa bakwai ne suka gana a ranar Lahadi inda suka zabi mutumin da bai zama fitacce ba Martin Fayulu a matsayin wanda zai daga tutar kawancen adawa a zaben da aza a yi ranar 23 ga watan Disamba.