1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jawabin shugaba Bashar Al-Assad

January 6, 2013

Shugaban Siriya ya ce ba zai hau teburin shawara ba da " 'yan amshin shatan ƙasashen ƙetare".

https://p.dw.com/p/17Epi
Syria's President Bashar al-Assad speaks at the Opera House in Damascus in this still image taken from video January 6, 2013. REUTERS/Syrian TV via Reuters TV (SYRIA - Tags: POLITICS PROFILE TPX IMAGES OF THE DAY) NO SALES. NO ARCHIVES. FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS IMAGE HAS BEEN SUPPLIED BY A THIRD PARTY. IT IS DISTRIBUTED, EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS. SYRIA OUT. NO COMMERCIAL OR EDITORIAL SALES IN SYRIA
Hoto: Reuters

Shugaba Bashar Al-Assad na Siriya ya gabatar da dogon jawabi, wanda a cikin sa ya taɓo batutuwa da dama da su ka haɗa da gwagwarmaya da wanda ya kira 'yan ta'ada.

Gaban dubunan magoya baya da ke taɓa masa, shugaba Assad ya yi kira g al'uma su ƙara ɗaura ɗamara yaƙi ,domin yaƙar 'yan tawaye da ya dangata da 'yan amshin shatar ƙasashen ƙetare.

"Muna da shaidu cikkaku na cewar da dama daga masu kiran su mazajen juyin juya hali, membobin Alqa'ida ne"

Saidai a ɗaya hannun, Assad ya ce a shirye ya ke ya tattauna da ƙungiyoyin tawayen dake buƙata, bayan yaƙi ya ƙare,amma banda masu karɓar umurni daga waje.

Sannan a shirye ya ke ya girka gwamnatin haɗin kan kasa, amma ta hanyar yin amfani da dokokin da ƙasa su ka tanada.

Shugaban Siriya ya isar da godiya ta mussamman ga ƙasashe Rasha, China da Iran ,wanda suka ba shi haɗin kai a cikin wannan gwagwarmaya.

Kusan shekaru biyu kenan da Siriya ta faɗa cikin mummuman rikic

Tuni ƙasashen duniya sun fara maida martani ga wannan jawabi.Kungiyar EU ta ce sam ba za ta wiwu ba a girka gwamnatin riƙwan ƙwarya tare da Assad, a yayin da shi kuma ministan harkokin wajen Birtaniya ya dangata jawabin da rashin imani

Yaƙin Siriya kawo yanzu a cewar Majalisar Dinkin Duniya ya haddasa mutuwar mutane fiye da dubu 60.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Umaru Aliyu