An zargi China da yiwa al'umma barazana
August 15, 2019Talla
Merkel ta kuma kara da cewar a baya yankin na Hong Kong ya yi fice wajen baiwa mazaunansa 'yancin bayyana ra'ayinsu, daga nan sai ta bayyana takaicin game da yadda rikici ya samu gurin zama tsakanin mazauna da mahukuntan yankin cikin takaitaccen lokaci.
Yanzu haka dai jami'an tsaron kasar China tare da manyan motocin yaki na atisaye a kudancin birnin Shenzhen cikin shirin yanki, lamarin da ya fusata mazauna Hong-Kong tare da janyowa gwamnatin China wacce ta tsuke bakinta game da wannan danbarwa Allah wadai daga bangarori da dama.