Hana bayar da kudade ga Masallatai a Jamus
December 29, 2018Talla
Jamus din ta ce ta umarci hukumomin tsaron ciki da wajen kasar da su sanya ido kan shige da ficen kudade a kasar tare da bukatar kasashen na Larabawa su sanar da mahukuntan Taraiyar ta Jamus a duk lokacin da wa ta kungiyar addini ta bukaci taimako daga garesu. Wannan mataki dai ya samo asali ne a yayin da ministan harkokin cikin gidan kasar Horst Seehofer ya gabatar da jawabi a lokacin babban taron Addinin Musulunci da aka gudanar a watan Nuwamban wannan shekarar a Jamus din, inda ya nemi kasashen ketare su daina shiga harkokin gudanarwar Masallatai a Jamus.