1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Ramaphosa na fuskantar zargi

Zulaiha Abubakar
October 10, 2018

Babbar jam'iyya adawa a kasar Afirka ta Kudu ta bukaci hukumar yaki da cin hanci ta binciki shugaba Cyril Ramaphosa da jami'an gwamnatinsa bayan ministan kudin kasar ya ajiye aiki.

https://p.dw.com/p/36IRQ
Südafrika Mahikeng Auschreitungen Cyril Ramaphosa
Hoto: Getty Images/AFP/M. Safodien

Ajiye aikin ministan kudin ya biyo bayan sanarwar ganawarsa da iyalan Gupta wadanda ake zargi da satar kudaden kasar a lokacin mulkin tsohon shugaban kasa Jacob Zuma.Yayin da yake rattaba hannu kan bukatar ajiye aikin ministan shugaban kasar ya jaddada wa al'ummar kasar aniyarsa ta yakar cin hanci lamarin da ya janyo wa tattalin arzikin kasar karewa , 'yan  jam'iyyar adawa dai na ci gaba  da kiraye-kirayen sai shugaba Ramaphosa ya bayyana wa al'ummar kasar bayanan da yake da su a  game da karkatar da kudaden gwamnatin da yayi sanadiyyar saukar tsohon shugaban kasar daga kujerar mulki.

Tuni fadar shugaban kasar ta sanar da Titö Mboweni tsohon shugaban bankin kasar a matsayin sabon ministan kudin kasar lamarin da 'yan adawa suka yi Allah wadai da shi.