Hukumar kare bil'Adama ta ce 'yan doka na kashe jama'a
April 16, 2020Talla
A cikin wani rahoton da ta wallafa a yammacin jiya, hukumar kare hakin bil'Adama ta Najeriya ta ce mutane akalla mutun 105 ne jami'an tsaron Najeriya suka ci wa zarafi haka ba tare da shari'a ba a yayin da wasu 18 suka mutu a yunkurinsu na tabbatar da doka da oda ga matakin takaita zirga-zirga da hukumomin Najeriya suka kakaba.