1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Dakarun gwamnati sun samu nasara Afirka ta Tsakiya

February 12, 2021

Gwamnatin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ta sanar a ranar Alhamis cewa sojojinta bisa gudummawar Rasha da Ruwanda sun yi nasarar 'yanto wani garin kan iyaka da ke yammacin kasar daga hannun hannun 'yan tawaye. 

https://p.dw.com/p/3pFaH
Zentralafrikanische Republik Premierminister Firmin Ngrebada
Hoto: Press Offive Prime Minister Central African Republic

A cikin sanarwar da firaministan kasar ya fitar ya ce nasarar ceto garin mai suna Beloko daga hannun kawancen 'yan tawayen kasar a yanzu ta ba su damar bude babbar hanyar da ta hada kasar ta Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da kasar Kamaru, yana mai cewa za su tabbatar jama'a na zirga-zirga cikin kwanciyar hankali.

Kungiyoyi masu rike da makamai akalla guda shida ne dai a kasar suka hada karfi suke yakar gwamnatin kasar tun a watan Disambar da ya gabata, kuma duk da cewa dakarun gwamnati sun samu nasarori, har kawo yanzu rahotanni na cewa 'yan tawayen sune ke da iko da kaso biyu cikin uku na kasar ta Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.